Ministar gwamnatin Buhari Sadiya Farouq za ta bayyana a gaban EFCC

top-news


Daga shafin BBC Hausa 

Rahotonni sun ce ministar jin-ƙai a gwamnatin Muhammadu Buhari, Sadiya Umar Farouq, za ta bayyana a ofishin hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya EFCC, bisa zargin almundahanar naira biliyan 37.

Bayanai sun ce a makon jiya ne hukumar ta aika wa tsohuwar ministar goron gayyata sakamakon wani bincike da hukumar ta ƙaddamar a kan aikace-aikacen ma'aikatarta lokacin da take riƙe da muƙamin tsawon shekara shida.

Ana bincikenta ne a kan zargin hannu a badaƙalar halasta kuɗin haram na fiye da naira biliyan 37 da miliyan 170, da wani ɗan kwangila James Okwete ya aikata.

NNPC Advert

Wata majiya a EFCC ta tabbatar wa BBC cewa ba shakka hukumar ta gayyaci tsohuwar ministar amma bai yi wani ƙarin haske ba.

Sadiya Umar Farouq ta fitar da wata sanarwa a ranar Litinin cikin makon jiya tana musanta zargin hannu a badaƙalar da ake zargin James Okwete da aikatawa, ta jaddada cewa ba ta ma san mutumin da ake magana a kansa ba.

Jaridar Punch ta ce tuni hukumar EFCC ta gayyaci ƙarin jami'ai da suka yi aiki da Sadiya don samun ƙarin haske a kan yadda ma'aikatar ta tafiyar da al'amuranta a cikin shekara shida.